IQNA

Jakadan Rohingya A Masar:

Firayi Ministar Myanmar Ita Ce Hirler A Wannan Zamani

17:22 - September 13, 2017
Lambar Labari: 3481892
Bangaren kas ada kasa, jakadan msuulmin Rohingya akasar Masar ya bayayna cewa, firayi ministan kasar Myanmar it ace Hitler a wannan zamani da muke ciki.

Kamfanin dillanacin labaran iqna ya habarta cewa, Umar Faruk jakadan musulmin Myanmar a kasar Masar ya bayyana cewa, a lokutan baya har zuwa shekara ta 1800 musulmi ne suke iko da yankin Rakhin, inda su ne suke da hakkin nada sarakunan yankin, amma daga lokacin zuwa gwamnatin Burma a cikin shekara ta 1973, daa lokacin aka fara cutar da musulmi tare da mayar da su saniyar ware.

Ya ce duk da cewa adadin musulmin Rohingya ya haura miliyan biyu da rabi a halin yanzu, amma adadin wadanda aka kasha daga fara kaddamar da ahri a kansu a cikin shekara ta 2016 ya zuwa yanzu, ya haura dubu biyar.

Umar Faruk y ace Aung Suu Kyi ita ce a matsayin Hitler ta wannan zamani.

3641402


captcha