IQNA

Wasu Daga Hotunan Musulmin Myanmar

17:32 - September 18, 2017
Lambar Labari: 3481909
Bangaren kasa da kasa, kungiyar Amnesty International ta nuna wasu daga cikin hotunan da aka dauka ta hanyar tauraron dana dam dangane da halin da musulmin Myanmar suke ciki.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, jaridar Guardian ta buga wani rahoto da ke bayyana irin mawuyacin halin da al'ummar musulmi suke cikia kasar Myanmar, da hakan ya hada har da hotunan da ke nuna yadda aka kone kauyukansu da gidajensu.

Wannan rahoto y ace fiye da mutane dubu 400 ya zuwa suka tsallaka cikin kasar Bangaladesh, yayin da wasu dubban kuma suka mutu ta hanyar kisan da sojoji da kuma 'yan addinin buda suke yia kansu, wasu kuma sun mutu a hanya, wasu kuma sun nutse a cikin ruwa.

Halin da musulmin Myanmar suke ciki yan ata kara munana sakamakon rashin samun wadataccen abinci da kuma kayan bukatar rayuwa a cikin sansanonin da aka tsugunnar da su.

3643200


captcha