Bayanin ya ci gaba da cewa, wannan taro yana daga cikin tarukan addinin muslunci da wannan cibiya take siryawa, domin raya lamarin iyalan gidan manzon Allah (SaW).
An gabatar da jawabai dangane da matsayin Imam Ridha (AS) da kuma darussan da suke a cikin rayuwarsa mai albarka ga dukkanin al’ummar musulmi.