Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na aabbir.com cewa, a jiya an nuna fin din nuna kyama da batunci ga addinin muslunci a gidan talabijin din gwamnatin kasar Holland da suna 'yancin fadar albarkacin baki.
Wannan lamari ya zo ne a daidai lokacin da jam'iyyar nan mai tsananin adawa da musulunci take ta kara fadada ayyukanta na nuna kyama da kuma cin zarafi da batunci ga musulmi a kasar.
Gwamnatin Holland ta amince ta watsa wannan fim din ne da sunan bayar da damar fadar albarkacin baki ko bayyana ra'ayi a tsakanin 'yan kasa.
Masu rajin kare hakkokin 'yan adam a kasar da dama sun yi tir da Allah wadai da wannan mataki da gwamnatin Holland ta bayar, na cin zarafin addinin muslunci a hukumance a kasar.