IQNA

Jagora: Iran Ta Sami Nasarar Dakile Makircin Amurka A Gabas Ta Tsakiya

17:48 - March 22, 2018
Lambar Labari: 3482498
Bangaren kasa da kasa, Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya bayyana cewar Iran ta sami nasarar dakile makircin Amurka a yankin Gabas ta tsakiya da kuma rage sharrin kungiyoyin 'yan ta'addan Takfiriyya daga kan al'ummomin yankin.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa,

Jagoran juyin juya halin Musuluncin ya bayyana hakan ne a wani jawabi da yayi a yammacin jiya a birnin Mashad na kasar Iran don tunawa da ranar farko na sabuwar shekarar hijira shamsiyya inda ya ce a shekarar da ta wuce din, Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta sami nasarar daga tutar daukaka da tsayin dakan al'ummar Iran a yankin Gabas ta tsakiya, sannan kuma ta taka gagarumar rawa wajen karya lagon kungiyoyin 'yan ta'adda masu kafirta mutane da kuma tabbatar da tsaro da zaman lafiya a yankin Gabas ta tsakiyan.

Yayin da yake magana kan makircin Amurka a yankin Gabas ta tsakiya, Ayatullah Khamenei ya bayyana cewar: Manufar Amurka ta kirkiro kungiyoyi ashararanci irin su Da'esh (ISIS), ita ce gwara kan al'ummomin yankin Gabas ta tsakiya da hada su fada da junansu, da nufin kautar da hankulansu daga haramtacciyar kasar Isra'ila, to sai dai Iran ta sami nasarar dakile wannan makircin.

Har ila yau kuma yayin da yake watsi da zargin da Amurka  da kawayenta suke yi wa Iran na tsoma baki cikin harkokin cikin gidan kasashen yankin Gabas ta tsakiyan kuwa, Jagoran juyin juya halin Musuluncin ya ce Iran ta shiga wadannan kasashen ne, bisa bukatar taimako da gwamnatocin kasashen suka gabatar mata, inda ta taimaka musu wajen tabbatar da tsaro da kuma fada da kungiyoyin ta'addancin da aka shigo da su kasashen.

Bisa ga al'ada dai a kowace shekara jagoran juyin juya halin muslunci yana kai ziyara a hubbare mai tsarki da Mashhad domin ganawa da al'aumma, inda a nan ne yake yin bayani na sabuwar shekara ga al'ummar kasa baki daya.

3701615

http://iqna.ir/fa/news/3701615

captcha