Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Al-Kauthar cewa, a karshen matakin karshe na gasar da aka gudanar a daren idin karamar sallah, an sanar da babban malamin kasar Iran Mustafa Hammet Ghasemi a matsayin wanda ya lashe gasar karo na 17 na Gasar kur'ani "Mufaza" da maki 87.25.
Haka kuma Mustafa Heydari daga Afghanistan da maki 86.5 da Mohammad Reza Al-Haj Uman daga Indonesia da maki 86.25 da Abdul Hossein Sweidan daga Jamus da maki 84.5 da Hassan Shaker Hamoud Al-Saadi daga Iraqi da maki 84 ya samu matsayi na biyu zuwa na biyar.
An fara gudanar da gasar karatun kur'ani mai tsarki karo na 17 na kasa da kasa mai suna "Mafaza" a daren farko na watan Ramadan inda aka ci gaba da gudanar da gasar har zuwa daren lailatul Fitr.
Ana watsa wadannan gasa a kowane dare a tashar Al-kawthar da gidan yanar gizon ta, da kuma shafin Al-kawthar a shafukan sada zumunta.